Africa academy

Ita ce makaranta irinta ta farko, da ake nazarin Musulunci, kyauta, kuna daga gida, cikin harshen Hausa

Muna da tsarin karatu iri biyu:

Gajerun kwasa-kwasai waɗanda suke ɗaukar batutuwan da suka shafi musulmi

Diplomar nazarin Musulunci, wacce ake yi cikin shekara ɗaya

Diplomar Nazarin Musulunci

Ɗalibi zai yi karatu kyauta, yana daga gida, na tsawon shekara ɗaya, inda zai karanci maddoji 12, a cikin zangon karatu biyu, waɗanda suka yi nasarar gamawa; za a ba su takardar shaidar kammalawa ta Africa academy.

Maddojin da ake karantawa

Aƙida

da Tafsiri

da Hadisi

da Fiƙih

da Sira

da Tarbiyyar Musulunci

Gajerun kwasa-kwasai

Wasu kwasai-kwasai ne da ake ilimantar da musulmai abin da ya shafi Addini, inda muke ɗaukar wani abu daga cikin abubuwan da ya wajaba kowane musulmi ya sani, sannan a ƙarshen kwas ɗin duk wanda ya ci jarrabawa; za a ba shi takardar shaidar kammalawa.

Ƙididdigar Africa academy

Ƙididdigar Africa academy

1

Yawan satifiket

1

Yawan kasashe

1

Yawan wadanda suka yi rijista

1

Yawan maza

1

Yawan mata

Masu koyarwa

Dr. Yusha_u Hanafi

Dr. Habeeb Tijjani Tahir

Shkh. Alkali Murtadha Al-Misry

Dr. Abdulƙadir Isma_il

Dr. Abubakar M. Birnin-Kudu

Shkh. AbdulMuɗɗalib Awwal Gusau

Dr. Nazifi Inuwa

Ra`ayin ɗalibai

5/5
Kwas ɗin nan yana da amfani, da sauƙi, ya sauƙaƙa mini fahimtar ilimin shari’ar Musulunci, kuma ya zaburar da ni, ta hanyar ba ni takardar shaidar karatun da ta dace, Allah Ya datar da ku, Ya kuma saka muku da alheri.
Ɗalibarku/ Makka Nur.
5/5
Cikin ɗan ƙanƙanin lokaci na fa’idantu sosai, na samu ƙarin ilimin addini ƙwarai da gaske. Allah Ya datar da ku, Ya kuma saka muku da alheri. .
Ɗalibarku, Sa’adatu Sa’id
5/5
Yayana ina matuƙar farin ciki, domin kwasa-kwasan nan sun ƙara mana ƙwarin guiwa, kuma suna taimaka mana wajen koyon addini, kuma muna kafa hujja a wajen da ya dace.
Ɗalibarku, Na’ima Abdullahi